DRC Congo-Rwanda
Sojojin Congo da Rwanda suna fada akan iyaka
Rahotanni Daga kasar Jamhuriyar Demokradiyar Congo sun ce an samu barkewar sabon fada akan iyakar kasar da Rwanda. Wani shaidar gani da ido yace an yi musayar wuta tsakanin bangarorin biyu da muggan makamai, bayan fadan jiya wanda ya yi sanadiyar kashe sojoji hudu. Kasar Congo ta zargi Rwanda da sace mata soja tare da hallaka shi, lamarin day a yi sanadiyar haifar da sabon rikicin tsakanin kasashen biyu.
Wallafawa ranar:
Talla
Rahotanni sun ce Sojojin Rwanda sun kashe Sojojin Congo guda biyar yayin da ko wane bangare ke zargin dayan da haddasa fadan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu