Isa ga babban shafi
Najeriya

Sojin Najeriya sun ce sun kashe ‘Yan Boko Haram 20 a Mafa

Rundunar sojin Najeriya tace Sojojinta sun kashe Mayakan Boko Haram 20 a yankin Mafa a Jahar Borno wannan kuma na zuwa ne bayan Gwmanatin Tarayya ta rufe makarantu a yankin arewa maso gabaci domin kaucewa hare haren da ake kai wa dalibai.

Jami'an tsaron Najeriya a garin Maiduguri.
Jami'an tsaron Najeriya a garin Maiduguri. AFP
Talla

A cikin Sanarwar da Kakakin rundunar Sojin kasar Chris Olukolade ya fitar yace sun mamayi mayakan ne a harin kwantar bauna a ranar Laraba a yankin Mafa da ke cikin Jahar Borno.

“Mayaka Ashirin ne suka mutu” a cewar Olukolade a cikin sanarwar.

A ranar Lahadi akalla mutane 29 aka kashe a Mafa bayan wasu hare haren bama bamai guda biyu da aka kai a Maiduguri da ya yi sanadin mutuwar mutane 35 inda wani harin kuma ya yi sanadiyar mutane 39.

Sanarwar Sojin na Najeriya na zuwa ne bayan Ma’aikatar Ilimi a Najeriya ta bayar da umurnin rufe wasu makarantun Gwamnati a Jahohin Yobe da Adamawa da Borno.

Akalla mutane 45 suka mutu a wani hari da mayakan Boko Haram suka kai a wata Makarantar Sakandare ta gwamnati a Buni Yadi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.