Isa ga babban shafi
Nigeria

MEND ta dauki alhakin kai hari kan 'yan sanda a Bayelsa

Kungiyar fafutukar kare yankin Niger Delta a Najeriya MEND, ta dauki alhakin kai hari kan wasu jiragen ruwan sintirin ‘yan sanda 2 a ranar asabar da ta wuce a jihar Bayelsa.

Mayakan MEND a Najeriya
Mayakan MEND a Najeriya AFP/PIUS UTOMI EKPEI
Talla

A sanarwar da ta aike wa kafafen yada labarai, kungiyar ta ce ta kai harin ne a yankin Perembari da ke kudancin karamar hukumar mulkin Ijaw saboda jiragen na dauke da wani mai suna Eris Paul daya daga cikin tsoffin jami’anta da a yau ta ke kallo a matsayin maciyi amana.

Har ila yau kungiyar ta ce harin ya yi kama da wanda ta taba kai wa a ranar 6 ga watan Afrilun shekarar 2013 inda ta kashe ‘yan sanda 15 da ke sintiri a yankin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.