Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya

Dubban mutane na tserewa daga Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya

Dubban mutane ne suka tsere daga yankunan da sabon rikici ya barke tsakanin tsoffin ‘yan tawaye da mayakan sa kai a Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya, lamarin da ya sa ake fargabar barkewar rikicin addini a kasar. 

'Yan tawayen kungiyar Seleka suna sintiri a kan titin birnin Bangui
'Yan tawayen kungiyar Seleka suna sintiri a kan titin birnin Bangui REUTERS/Alain Amontchi
Talla

Kasar ta shiga rudani tun bayan da mayakan na Seleke suka karbe ikon babban birnin Bangui suka kuma jingine gwamnatin Francois Bozize a watan Maris.

Shugaban ‘yan tawayen Michel Djotodia ya nada kansa a matsayin shugaban rikon kwaryar kasar tare da rushe hadakar kungiyoyin ‘yan tawaye da suka gaza wajen kare rikici tskanin mayakan sa kai.

Sabon rikicin ya barke ne a kudancin garin Bouca kilomita 290 daga arewacin birnin Bangui.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.