Isa ga babban shafi
Faransa-Mali

Ana zargin ‘Yan tawayen Abzinawa ne suka kashe Ma’aikatan RFI

Mai Gabatar da kara a kasar Faransa, Francois Molins, ya bayyana sunan Baye Ag Bakabo, daya daga cikin shugabanin Abzinawan Mali, a matsayin wanda ke da hannu wajen kashe ma’aikatan Rediyo Faransa biyu, Claude Verlon da Ghislaine Dupont. Jami’in yace an samu shaida a cikin motar da aka sace ‘Yan Jaridun da ke dauke da sunansa, kuma an ganshi yana tuka motar.

'Yan kasar Mali suna zanga-zangar adawa da kisan Ma'aikatan Gidan Rediyo Faransa RFI
'Yan kasar Mali suna zanga-zangar adawa da kisan Ma'aikatan Gidan Rediyo Faransa RFI RFI/Pierre -René Worms
Talla

Molins ya kara da cewar, wani kwamandan kungiyar Al Qaeda, Abdelkarim al Targui ne ya bayar da umurni sace ‘Yan Jaridun, a matsayin ramako kan yadda sojojin Faransa da Majalisar Dinkin Duniya suka kakkabe Yan Tawayen kasar a yankin arewaci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.