Isa ga babban shafi
Mali

Jami’an tsaron Mali na ci gaba da tuhumar mutane tara game da kisan wakilan rfi

Jami’an tsaro a kasar Mali na cigaba da yiwa wasu mutane tara tambayoyi daga cikin wadanda ake zargin suna da hannu wajen kashe ‘Yan Jaridun Radio Faransa biyu, Claude Verlon da Ghislaine Dupont. 

Claude Verlon (tsakiya) da Ghislaine Dupont (dama) a lokacin da suke aiki a Mali
Claude Verlon (tsakiya) da Ghislaine Dupont (dama) a lokacin da suke aiki a Mali RFI/Pierre René-Worms
Talla

Jami’an tsaron sun kuma gano mai motar da aka yi anfani da ita wajen sace ‘yan Jaridun kafin a hallaka su, inda aka bayyana sunansa a matsayin Ag Bakabo.

Ag Bakabo na daga cikin 'yan Tawayen Abzinawa dake neman kasa ta kansu wadda ake cewa tana da alaka da kungiyar Al Qaeda.

A makon da ya gabata ne aka kashe ‘yan jaridun biyu bayan sun kammala aiki a garin Kidal dake arwacin kasar ta Mali.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.