Jamhuriyyar Congo
Dakarun Congo sun kwace garuruwa biyu daga hannun ‘Yan tawaye
Sojojin Jamhuriyar Demokradiyar Congo sun ce sun kama karin garuruwa biyu da suka fada hannun ‘Yan Tawaye, yayin da suka kama hanyar zuwa Rutshuru, a wata alamar samun nasarar dakarun gwamnati. Col Olivier Hamuili, mai Magana da yawun rundunar sojin kasar, yace suna kama hanyar kama garin Rutshuru, amma za su karbi aje makaman wadanda suka bada kai, kuma za su abkawa wadanda suka ki. Yau an shiga rana ta 4 na fafatawar da ake tsakanin sojojin gwamnati da ‘Yan Tawayen.
Wallafawa ranar: