Isa ga babban shafi
Cote d'Ivoire

Ble Goude ya nemi kada a mika shi zuwa ICC

Shugaban Kungiyar ‘Yan ina da kisa Charles Ble Goude a karkashin tsohuwar gwamnatin kasar Cote d’Ivoire, ya bukaci gwamnatin kasar da kar ta mika shi ga kotun hukunta manyan laifuka don fuskantar shari’ar kisan kai da fyade, yana me bukatar a yi masa shari’a a gida. Lauyan wanda ake zargin, Claver N’Dri, yace sun mika bukatarsu ga gwamnatin kasar, na ganin an yi wa Ble Goude shari’a a gida, saboda imanin da suke da shi cewar kotunan kasar za su iya yin adalci.

Charles Blé Goudé na Cote d'Ivoire
Charles Blé Goudé na Cote d'Ivoire REUTERS/Thierry Gouegnon
Talla

Ble Goude wanda shi ne na hannun damar Gbagbo ana zarginsa ne da mallakar wata kungiya da ta kashe mutane kusan 3,000 da ke adawa da shugaban kasa na yanzu Alassane Ouattara.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.