Uganda
Human Rights Watch ta koka da matakan da Uganda ke dauka
Kungiyar Kare Hakkin Bil Adama ta Human Rights Watch, tace gwamnatin kasar Uganda ta kasa hukunta manyan jami’an da ake zargi da cin hanci da rashawa a cikin kasar, amma kuma tana cigaba da garkame wadanda suke tona asirin wadanda ake zargin.Kungiyar tace, har ya zuwa yau babu wani babban jami’in gwamnati ko Ministan da aka daure kan zargin cin hanci, duk da yake an samu wasu da dama da suka yi dumu dumu da dukiyar talakawa.Kungiyar tace, kudin agaji da ake baiwa kasar da suka kai kusan Dala biliyan 13 jami’an gwamnati suka sace, ba tare da an hukunta su ba.
Wallafawa ranar: