Mali: Boubacar Keita ya sha alwashin sake hada kan ‘yan kasar
Zababben Shugaban kasar Mali, Ibrahim Boubacar Keita, ya dauki aniyar sake hada kan ‘Yan kasar, daga matsalar siyasa, juyin mulki da kuma yakin da ya rarraba kawunansu.
Wallafawa ranar:
Duk da yake ana cigaba da dakon sakamakon zabe daga hukumomin kasar, tuni Soumaila Cisse, ya amsa shan kaye, kuma ya yi tattaki zuwa gidan Keita inda ya taya shi murna.
Shugaban kasar Faransa, Francois Hollande ya bayyana farin cikinshi da zaben, inda ya sanar da aniyar sa na halartar bikin rantsar da sabon shugaban.
A ranar Lahadin da ta gabata ne aka sake gudanar da zabe a zagaye na biyu bayan ‘yan takarar sun gaza samun kuri’u masu rinjaye.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu