Isa ga babban shafi
Masar

Kungiyar kasashen Turai ta nemi a saki hambararren shugaban kasar Masar Morsi

Babbar Jami’ar diflomasiyar kasashen Turai, Catherine Ashton, ta bayyana bacin ran ta na rashin ganawa da hambararen shugaban kasar Masar, Mohammed Morsi, lokacin da ta ziyarci kasar.

Jami’ar Diflomasiyar kasashen Turai, Catherine Ashton
Jami’ar Diflomasiyar kasashen Turai, Catherine Ashton REUTERS/Hamad I Mohammed
Talla

Jami’ar ta bukaci hukumomin kasar Masar, da su gaggauta sakin tsohon shugaban, wanda ta ce an shaida mata cewar yana cikin halin koshin lafiya.

Ashton ta bayyana hakan ne bayan ganawa da ta yi da sababbin shugabannin kasar ta Masar da kuma bagaren masu goyon bayan Morsi.

Wannan kira na zuwa ne a dai dai lokacin da ake ci gaba da nuna bore ga gwamnatin rikon kwaryar kasar ta Masar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.