Isa ga babban shafi
MALI-AU-NATO

An nada shugaban rundunar Majalisar Dinkin Duniya a Mali

Babban Magatakarda na Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki-Moon, ya nada Bert Koenders dan kasar Holland a matsayin shugaban rundunar wanzar da zaman lafiya ta Majalisar a kasar Mali.

Shugaban rundunar Majalisar Dinkin Duniya a Mali, Bert Koenders
Shugaban rundunar Majalisar Dinkin Duniya a Mali, Bert Koenders DR
Talla

Ita dai wannan runduna wadda za to soma aiki a ranar 1 ga watan Yulin wannan shekara, babban aikin da ya rataya a wuyanta shi ne kokarin dawo da tsaro a kasar mai fama da yakin basasa, sannan kuma za ta taka rawa domin samar da yanayin shiga tattaunawa tsakanin gamnati da kuma ‘yan tawayen kungiyar MNLA.
A can baya dai, Bert Koenders, ya taba rike mumakin shugaban rundunar MDD a kasar Cote d’Ivoire wato ONUCI, kuma rundunar da zai jagoranta a kasar ta Mali, za ta kunshi dakaru akalla dubu 12.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.