Harin bom a Somalia ya kashe mutane 11
Kungiyar Al Shabaab a kasar Somalia, ta kai harin kunar bakin wake kan tawagar jami’an kasar Kuwait dake ziyarar kasar. Harin a cewar rahotanni ya yi sanadiyar mutuwar muatne 11.
Wallafawa ranar:
Rahotanni sun ce, harin ya kuskuri tawagar motocin, kamar yadda wani shaidar gani da ido, Abdi Ayante ya shaidawa Radio Faransa.
“Abinda muka sani kawai shine motar kunar bakin wake, ta kai hari kan tawagar jami’an diplomasiya, kuma wadanan motoci Ministan cikin gida ya saba amfani da su, amma a wannan karon jami’an diplomasiyar Qatar, sai dai motar tana da sulken kare harsashi, abinda ya kare lafiyar su.”
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu