An samu fashewa a birnin Gao na kasar Mali
Wani abu ya fashe a Birnin Gao, da ya fi kowanne girma a Arewacin kasar Mali, sa’oi, bayan ‘Yan bindiga masu kishin Isalama sun yi fito-na fito da sojojin kasar da na Faransa.
Wallafawa ranar:
Wakilin Kamfanin Dillancin labarai Faransa na AFP, ya ce da alama Fashewar ta safiyar yau litinin ta faru ne a Arewacin kasar.
Kungiyar masu tsananin kishin Islama ta MUJAO, ta dauki alhakin hare haren da ‘Yan bindigar suka kai a birnin da suka biyo bayan kunar bakin waken da suka kai.
Lamarin na baya bayan nan, ya zo ne, wata daya, da fara fatattakar ‘Yan tawayen kasar da Faransa ke jagoranta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu