Isa ga babban shafi
Mali-Amnesty

Amnesty ta nemi a kiyaye rayuwar fararen hula a Mali

Kungiyar kare hakkin Bil’adama ta Amnesty International ta yi gargadin bangarorin da ke yaki a kasar Mali su tabbatar da sun kiyaye rayukan fararen hula da ke kasar a wata sanarwa da Kungiyar ta fitar sakamakon fara kai hare-hare ta sama da sojan kasar Faransa suka kaddamar a yankunan Arewacin kasar.

Wani Jirgin yakin Kasar Faransa a lokacin da zai sauka a birnin Bamako.
Wani Jirgin yakin Kasar Faransa a lokacin da zai sauka a birnin Bamako. AFP PHOTO / ISSOUF SANOGO
Talla

Kungiyar Amnesty tace akwai matukar damuwa game da halin da fararen hula za su shiga sakamakon rikicin Mali.

A cewar Paule Rigaud Darektan kungiyar mai kula da Nahiyar Afrika ba su fidda tsammanin za’a abkawa wadanda ba su san hawa ba ba su san sauka ba. Saboda haka suke neman a kiyaye.

Kungiyar tace tana da hakkin ganin babu wani muzgunawa da aka yi wa Bil’adama, kuma tana bukatar duniya ta mara masu baya domin a tura masu sa ido zuwa yankunan da ake rikicin domin ganin ba a wuce gona da iri ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.