Hollande ya isa Algeria domin dinke barakar da ke tsakaninsu da Faransa
Shugaban kasar Faransa Francois Hollande ya kai ziyarar kwanaki biyu a kasar Algeria domin farfado da dangantar da ke tsakanin kasar da Faransa tare da inganta huldar kasuwanci. Wannan ce ziyara ta farko da Hollande ya kai a Algeria bayan ya gaji Nicolas Sarkozy a lokacin da kasar ta gudanar da bukin cika shekaru 50 da samun ‘yancin kai daga Faransa.
Wallafawa ranar:
Francois Hollande zai gana da shugaba Abdelaziz Bouteflika kuma batutuwan da zasu tattauna sun hada da neman goyon bayan mahukuntan kasar Algeria su amince da daukar matakn soji a kasar Mali.
A watan Oktoba Shugaba Hollande ya amince da kisan gillar da ‘yan sandan Faransa suka yi wa al’ummar Algeria masu zanga-zangar neman ‘yanci a birnin Paris a shekarar 1961, inda masana tarihi suka ce daruruwan mutane ne suka mutu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu