Najeriya
‘Yan bindiga sun harbe wani Dan majalisar Jaha a Arewacin Najeriya
Wasu ‘Yan bindiga sun harbe wani Dan majalisar Jaha, a garin potiskum cikin Jahar Yobe da ke Arewacin Najeriya.
Wallafawa ranar:
Talla
‘Yan sandar Jahar sun bayyana cewa ‘Yan bindigar sun harbe Dan majalisar mai suna Adamu Deguri, a kofar gidansa da ke Unguwar Tandari a birnin Potiskum.
Bayanan da ‘Yan sandar su ka bayar, ya nuna cewa ‘Yan bindigar sun kai harin kan Dan majalisar ne a ciki wata mota kirar Bas, wacce ba ta lamba bayan sun bi shi a baya inda su ka bindige shi a yayin da ya ke kokarin fitowa a motarsa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu