Dubban mutane na komawa Aleppo
Dubban mutane na komawa gidajensu a birnin Aleppo na arewacin Syria, sakamakon zaman lafiyar da aka sama bayan da dakarun gwamnati suka kwace garin daga hannun ‘yan tawaye.
Wallafawa ranar:
Garin Aleppo wanda ke kunshe da kusan mutane miliyan biyu kafin barkewar yaki a Syria yanzu ya kasance kamar an yi ruwa an dauke sakamakon kazamin artabun da aka yi tsakanin ‘yan tawaye da kuma dakarun gwamanati a tsawon shekaru kusan shida.
A cikin wannan mako kawai sama da iyalai dubu biyu ne suka koma garin na Aleppo kamar dai yadda shugaban ofishin kula da ‘yan gudun hijira na Majalisar Dinkin Duniya a yankin na Aleppo Sajjad Malik ya tabbatar.
Jami’in ya ce mutane na ci gaba da komawa gidajensu, kuma an bude shaguna da dama a birnin, duk da cewa an lalata mafi yawa daga cikin gine-ginen da ke cikinsa.
Sai dai kamar yadda rahotanni ke cewa, jama’a na rayuwa ne a cikin mawuyacin hali, sakamakon sanyin huturu da kuma karancin makamashin wutar lantarki da kuma iskar gas, yayin da wasu ke rayuwar a cikin gidajen da ba su kofofi balantana taga.
Wata babbar matsalar da jama’ar birnin ke fuskanta a halin yanzu ita ce rashin ruwan sha mai tsafta.
A shekara ta 2012 ne dai ‘yan tawaye suka kama birnin na Aleppo, kuma sai a watan Disamban da ya gabata ne dakarun Bashar Assad tare da taimakon Rasha suka yi nasarar kwace birnin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu