Shugaba Keita ya jagoranci taron zaman lafiya kasar Mali
Shugaban Mali Ibrahim Boubacar Keita, a jiya asabar ya jagoranci taron zaman lafiyar kasar,Shugaban na Mali ya gayyaci daukacin kungiyoyin farraren hula na kasar, yan siyasa, da kungiyoyi dake dauke da makamai.
Wallafawa ranar:
Jam’iyoyin adawa sun kauracewa zaman taron da aka soma jiya a babban birnin kasar Bamako, inda aka bayyana akalla mutane dubu uku a zauren taron.
Taron, yunkurin ne na gwamnatin Mali wajen amfani da tattaunawar sulhu, don kawo karshe tashe-tashen hankula a sassan kasar na hare-haren masu ikirarin Jihadi, da rikicin kabilanci.
An dai soma tattaunawar zaman lafiyar ne watanni bayan fuskantar tashin hankalin a wasu yankunan kasar Malin wacce ta fuskanci hare-hare daga kungiyoyin yan ta’adda, abinda yayi sanadin salwantar rayukan dakarun kasar sama da 140.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu