Kotun kolin Liberia ta bayyana cewa za 'a gudanar da zagaye na biyu na zaben kasar
Kotun koli Liberia ta yi watsi da zargin da ake yi ne cewa hukumar zaben kasar ta tafka magudi a zagayen farko na zaben shugaban kasar da aka gudanar.
Wallafawa ranar:
Bayan jinkarta zagaye na biyu na zaben da ya kamata a fafata tsakanin Joseph Boakai na jam’iyyar mai mulki da George Weah a ranar 7 ga watan Nuwamba,a jiya alhamis kotun kolin Liberia ta bayyana cewa za a gudanar da zagaye na biyu na zaben Shugaban kasar.
Charles Brumskine na Jam’iyyar Liberty da ya zo na Uku a zaben ne ya shigar da korafin da ya yi sanadi jinkirta zaben.
Sai dai hukumar zaben kasar ta ce jam’iyyu da ke zargin an aikata magudi sun gaza gabatar da hujojjin da ke tabbatar da hakan.
Kafin wannan sanarwa, Jam’iyyun da suka shigar da kara sun bukaci jami’an hukumar zaben kasar suyi murabus.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu