Isa ga babban shafi
Guinea-Conakry

‘Yan adawa sun bukace a dage zaben Guinea

‘Yan adawa a kasar Guinea Conkry sun bukaci a dage gudanar da zaben shugabancin kasar da ya kamata a yi a ranar 11 ga wannan wata wannan oktoba da akalla mako daya, domin bai wa hukumar zabe damar kara kintsawa.

Shugaban kasar Guinea Conakry Alpha Condé.
Shugaban kasar Guinea Conakry Alpha Condé. AFP/CELLOU BINANI
Talla

A cewar Faya Francois Bruno, mai magana da yawun ‘yan adawar manyan dalilan su na dage zaben, sun hada da rashin kintsawa wannan zabe, raba katunan zabe bisa rashin tsari a kasar, kuma akwai dimbin jama’ar da suka yi rejista amma har zuwa wannan lokaci ba su samu katunansu.

Faya ya kuma kara da cewa Har ila yau suna da shakka a game da wasu kamfanonin daba’i da aka bai wa kwangilar buga katunan zabe.

Sannan akwai matsala dangane da yawan wadanda suka cancanci jefa kuri’a, a wasu rumfana za a tarar cewa akwai dimbin jama’a yayin da a wasu yankunan yawan masu kada kuri’a bai taka kara ya karya ba.

Abin da suka bayyana cewa ba su yarda da shi ba,Saboda haka suka bukaci a dage wannan zabe da akalla mako daya, domin gudanar da zabe cikin kwanciyar hankali a kasar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.