Dakarun gwamnatin Syria sun yi nasarar kwace ikon birnin Aleppo daga hannun Yan Tawaye, al’amarin da ake ganin gagarumar nasara ce da za ta taimaka wajen kawo karshen yakin kasar da aka kwashe shekaru 5 ana fafatawa.
Shugaban kasar Bashar al-Assad dai ya yi watsi da duk wani yunkuri na tsagaita wuta ko kuma tattaunawa da yan Tawayen maimakon hakan Assad ya ci gaba da anfani da karfi a yaki da ‘yan tawayen da suka yi sanadiyar mutuwar mutane sama da dubu biyu.
Batun nasarar kwace birnin Aleppo da kuma makomar kasar ta Syria ya sa Ramatu Garba Baba ta tattauna da Dr Elharoun Mohammed na kwallejin kimiyya a Kadunan Najeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu