Dakarun Chadi sun fatataki yan Kungiyar Boko Haram
Sojojin Chadi sun kaddamar da wani gagarumin farmaki akan mayakan Boko Haram a wasu kauyuka da ke kusa da tafkin Chadi kamar dai yadda shaidu suka sanar.Wannan nasara na zuwa ne yan kwanuki bayan da Rundunar sojan Nigeria ta 7 da ke Maiduguri ta ce dakarun kasar sun kwato garin Dikwa da ke jihar Borno, bayan da garin ya share watanni da dama a hannun ‘yan kungiyar boko haram.
Wallafawa ranar:
Rahotanni sun ce tun a jiya litinin ne dakarun na Chadi suka fara kai hare-haren a yankin da ke cikin kusurwar da ta hada iyakokin kasashen Nigeria, Niger, Kamaru da kuma Chadi, yankin da ake kallo a matsayin babbar maboyar magoya bayan Boko haram.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu