Isa ga babban shafi
Wasanni-Kwallon kafa

Dakatarwar shekaru 2: Manchester City za ta daukaka kara

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ta sha alwashin daukaka kara kan hukuncin UEFA na dakatar da ita daga shiga gasar cin kofin zakarun Turai na tsawon kakar wasa biyu bayan samunta da laifin kashe kudin da ya wuce kima wajen sayen sabbin ‘yan wasa.

Mai horar da kungiyar kwallon kafa ta Manchester City Pep Guardiola.
Mai horar da kungiyar kwallon kafa ta Manchester City Pep Guardiola. © REUTERS/Phil Noble
Talla

Cikin wata sanarwar gaggawa da Manchester City ta fitar jim kadan bayan hukuncin UEFA na dakatar da ita daga ga shiga gasar ta zakarun Turai har tsawon shekaru 2, kungiyar ta nuna rashin jin dadi da hukuncin yayinda ta sha alwashin daukaka kara.

A cewar sanarwar ta City hukuncin na UEFA bai zo mata da mamaki ba, amma ta yi fatan samun sassauci, bayan da hukumar ta sameta da kaiwa kololuwa wajen karya ka’idar kashe kudi wajen sayen ‘yan wasa.

Karkashin hukuncin na UEFA bayan biyan tarar yuro miliyan 30 Manchester City ba kuma zata fafata a gasar cin kofin zakarun Turai a kakar wasa ta 2020-2021 ba da kuma 2021-2022.

A cewar sashen da ke sanya idanu kan kashe kudin kungiyoyi wajen sayen ‘yan wasa karkashin hukumar ta UEFA, Manchester City ta kashe kudaden da suka wuce ka’ida tsakan-kanin shekarun 2012 zuwa 2016 wajen sayen ‘yan wasa, haka zalika Club din ya gaza bayar da hadin kai yayin binciken UEFA.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.