Isa ga babban shafi
Wasanni

Saudiya za ta fara gasar kwallon kafa ta mata zalla

Shugaban Hukumar Kwallon Kafa ta Spain Luis Rubiales ya bayyana cewa, za su taimaka wa Saudiya shirya gasar lig ta mata zalla, matakin da ke zuwa a daidai lokacin da Yarima Jiran Gado, Mohamed bin Salman ke bullo da sauye-sauye a kasar wadda a can baya aka sani da bin tsauraran dokokin Islama.

Wasu daga cikin matan Saudiya a filin wasa na Sarki Abdallah da ke birnin  Jeddah
Wasu daga cikin matan Saudiya a filin wasa na Sarki Abdallah da ke birnin Jeddah STRINGER / AFP
Talla

Rubiales ya bayyana haka a yayin da ake shirin gudanar da gasar Super Cup ta kwararrun kungiyoyin La Liga a birnin Jeddah na Saudiya nan da watan Janairu mai zuwa.

Kungiyoyin da za su fafata a wannan gasa sun hada da Barcelona da Real Madrid da Atletico Madrid da kuma Valencia.

Za a gudanar da wasannin ne a filin wasa na Sarki Abdallah mai daukar nauyin ‘yan kallo dubu 62 a birnin Jeddah.

Barcelona za ta kara da Atletico Madrid, yayin da Valencia ta fafata da Real Madrid kafin a gudanar da wasan karshe a ranar 12 ga watan na Janairu mai zuwa.

Yarima Mohamed bin Salman ya kawo sauye-sauye a Saudiya, inda ya dage dokar haramacin gudanar da wasannin kade-kade da raye-raye, yayin da kuma ya bude gidajen Sinima, baya ga bai wa mata damar fara tukin mota da kansu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.