Ana cece-kuce kan kyautar da FIFA ta bai wa Messi
Shirin Duniyar Wasanni na wannan makon tare da Abdurrahman Gambo Ahmad ya tattauna ne kan cece-kucen da ake ci gaba da yi dangane da kyautar da Hukumar Kwallon Kafa ta Duniya ,FIFA ta bai wa Lionel Messi a matsayin gwarzon dan kwallon bana. Da dama daga cikin wadanda suka kada kuri'ar sun yi korafin cewa, an tafka magudi a zaben, abin da ya haifar da shakku kan sahihancin zabukan da aka gudanar a can baya.