Isa ga babban shafi

UEFA ta fitar da sabon jadawalin gasar cin kofin zakarun Turai

Hukumar kwallon kafar Turai ta fitar da sabon jadawalin gasar cin kofin zakarun Turai, a wasannin gasar da za su fara daga 17 ga watan satumba mai kamawa zuwa ranar 30 watan Mayun 2020.

Tawagar kungiyar kwallon kafa ta Liverpool bayan lashe kofin zakarun Turai.
Tawagar kungiyar kwallon kafa ta Liverpool bayan lashe kofin zakarun Turai. REUTERS/Toby Melville
Talla

A rukunin farko na jadawalin wato rukunin A wanda ya kunshi kungiyoyin kwallon kafa 4 akwai PSG ta Faransa da Real Madrid da Club Bruges da kuma Galatasaray.

A rukunin B kuwa akwai Bayern Munich da Tottenham, da Olympiakos baya ga Red Star Belgrade.

Sai rukunin C da ya kunshi Manchester City da Shakhtar Donetsk da kuma Dinamo Zagreb baya ga Atalanta.

Akwai kuma rukunin D da ya kunshi Juventus da Atletico Madrid sai Bayer Leverkusen da kuma Lokomotiv Moscow.

Sai rukunin E da ya kunshi Liverpool mai rike da kambun na zakarun Turai sannan Napoli kana Salzburg, da Genk.

Akwai kuma rukunin F da hadar da Barcelona, Borussia Dortmund, da Inter Milan da kuma Slavia Prague.

Sai rukunin G da yakunshi Zenit St Petersburg da Benfica da Lyon da kuma RB Leipzig.

Kana rukunin H kuma na karshe da ya kunshi Chelsea, Ajax da Valencia kana Lille.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.