'Leroy Sane zai yi jinyar watanni shida zuwa bakwai'
Kocin Manchester City pep Guardiola na sa ran Leroy Sane zai rasa damar taka leda har tsawon watanni shida zuwa bakwai sakamakon raunin da ya samu a guiwar kafarsa.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Sane mai shekaru 23 ya gamu da raunin ne a yayin gasar Community Shield da Manchester City ta samu nasara akan Liverpool a Wembley a ranar Lahadin da ta gabata.
Dan wasan ya fice daga fili bayan shafe minti 13 kacal akan filin wasan na Wembley, yayinda ake sa ran yi masa tiyata a birnin Barcelona a mako mai zuwa.
Raunin Sane dan asalin Jamus na zuwa ne a daidai lokacin da ake fara sabuwar kakar gasar firimiyar Ingila, inda a gobe Asabar, kungiyarsa ta Manchester City za ta barje gumi da West Ham.
A cewar Guardiola, ba shi da masaniya game da tsawon jinyara da Sane zai yi, amma ya ce, irin wannan raunin na kaiwa watanni shida zuwa bakwai kafin warkewa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu