Ighalo ya yi gaggawar rataye takalmansa- Babangida
Tsohon fitaccen dan wasan Super Eagles, Tijjani Babangida ya bayyana cewa, Odion Ighalo ya yi gaggawar rataye takalmansa a matakin wasan kasa da kasa.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Ighalo da ya lashe kyautar takalmin zinari a Gasar Cin Kofin Kasashen Afrika da aka gudanar a Masar, ya sanar da ritayarsa daga buga wa Najeriya kwallon kafa.
Sai dai Tijjani Babangida ya bayyana cewa, yana da shakku game da sahihancin labarin ritayar Ighalo, amma muddin labarin ya zama gaskiya, to lallai ya kamata a dakatar da shi daga ritayarsa domin kuwa a halin yanzu babu wanda zai iya maye gurbinsa a tawagar Super Eagles.
Babangida ya bayyana Ighalo a matsayin kwararren dan wasan gaba da tauraronsa ke haskawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu