Isa ga babban shafi
Wasanni

Neymar ya musanta zargin aikata laifin fyade

Tauraron kwallon kafar Brazil, kuma na kungiyar PSG, Neymar, ya musanta zargin da wata mata ke masa, na yi mata fyade a Faransa.

Dan wasan kungiyar PSG Neymar.
Dan wasan kungiyar PSG Neymar. AFP /Lionel Bonaventure
Talla

Bayanan da jami’an ‘yan sandan Brazil suka fitar, ya ce matar ta kai musu rahoton cewa cin zarafin ya auku ne a wani Otal da ke babban birnin kasar ta Faransa wato Paris.

Matar wadda yan sandan basu bayyana sunan ta ba, ta ce, ta soma haduwa da Neymar ne ta shafin Instagram, daga bisani kuam suka shirya haduwa a Paris, dan wasan kuma ya biya mata kudin jirgi.

Matar ta kara da cewa bayan haduwarsu ne Neymar ya ci zarafinta, yayinda yake cikin maye kamar yadda ta yi ikirari.

Sai dai cikin jawabin da yayi na tsawon mintuna 7 ta shafinsa na Instagram, Neymar ya yi watsi da zargin wanda ya bayyana shi da yunkuri na bata masa suna.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.