Isa ga babban shafi
Wasanni

Hankalin Liverpool ya koma kan kofin zakarun Turai

Kocin Liverpool, Jurgen Kloop ya kalubalanci ‘yan wasansa da su yi amfani da radadin rashin lashe kofin gasar firimiya ta Ingila a matsayin wani kaimi da zai taimaka musu lashe kofin zakarun Turai a bana.

Magoya bayan Liverpool sun yi takaicin gaza lashe kofin firimiya na Ingila
Magoya bayan Liverpool sun yi takaicin gaza lashe kofin firimiya na Ingila Reuters/Carl Recine
Talla

Liverpool ta kammala gasar firimiya ta bana da banbacin maki guda tsakaninta da Manchester City wadda ta sake lashe kofin a bana.

Liverpool ta kammala gasar ne da maki 97, yayinda Manchester City ta kammala da maki 98.

Kodayake Liverpool ta samu nasara a karawar da ta yi da Wolves da ci 2-0, amma hakan bai yi tasiri ba ko kadan, lura da cewa, Manchester City ta doke Brighton da ci 4-1, abinda ya haramta wa Liverpool din daga kofin firimiya a karon farko cikin shekaru 29.

Yanzu haka Liverpool ta mayar da hankalinta kan lashe kofin gasar zakarun Turai, in da za ta kara da Tottenham a wasan karshe a birnin Madrid a ranar 1 ga watan gobe.

A bangare guda, kocin Manchester City, Pep Guadiola ya bayyana cewa, kare kambin gasar firimiyar Ingila a wannan shekara, shi ne lokaci mafi wahala a gare shi a tarinhinsa na kwallon kafa.

A cewar kocin, sake lashe kofin bai zo musu da sauki ba, musamman ganin yadda suka barje gumi a wasanni 14 da suka samu nasara a jere.

Guardiola dai ya lashe kofin gasar La Liga sau uku a jere a lokacin da yake jagorancin Barcelona a Spain, sannan kuma ya sake lashe kofin Bundesliga sau uku a jere a lokacin da yake Bayern Munich ta Jamus.

A yanzu kocin na fatan a badi ya sake lashe kofin firimiyar Ingila, wanda hakan zai kasance sau uku kenan a jere da zai lashe kofin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.