Isa ga babban shafi
Wasanni

Giroud ya bayyana shirin rabuwa da Chelsea

Dan wasan gaba na Chelsea, Olivier Giroud, ya ce a shirye yake ya rabu da kungiyar a karshenkakar wasa ta bana, saboda matsalar da yace yana fuskanta ta ki bashi damar buga wasanni, karkashin kocin kungiyar ta Chelsea Maurizio Sarri.

Dan wasan gaba na Chelsea Olivier Giroud.
Dan wasan gaba na Chelsea Olivier Giroud. Reuters/John Sibley
Talla

Kalaman dan wasan na zuwa a dai dai lokacin da rahotanni ke cewa kungiyar Marseille da ke gasar League 1 ta Faransa na nemansa.

Giroud mai shekaru 32, ya soma zaman dumama benci ne bayan zuwan da Gonzalo Higuain yayi a matsayin aro daga kungiyar AC Milan.

Tauraruwar dan wasan na Giroud ta soma haskawa ne a shekarar 2012, bayan taimakawa kungiyar Montpellier lashe kofin gasar League 1 ta Faransa, inda a shekarar Arsenal ta saye shi, a watan Janairu na 2018 kuma dan wasan ya koma Chelsea.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.