Giroud ya bayyana shirin rabuwa da Chelsea
Dan wasan gaba na Chelsea, Olivier Giroud, ya ce a shirye yake ya rabu da kungiyar a karshenkakar wasa ta bana, saboda matsalar da yace yana fuskanta ta ki bashi damar buga wasanni, karkashin kocin kungiyar ta Chelsea Maurizio Sarri.
Wallafawa ranar:
Kalaman dan wasan na zuwa a dai dai lokacin da rahotanni ke cewa kungiyar Marseille da ke gasar League 1 ta Faransa na nemansa.
Giroud mai shekaru 32, ya soma zaman dumama benci ne bayan zuwan da Gonzalo Higuain yayi a matsayin aro daga kungiyar AC Milan.
Tauraruwar dan wasan na Giroud ta soma haskawa ne a shekarar 2012, bayan taimakawa kungiyar Montpellier lashe kofin gasar League 1 ta Faransa, inda a shekarar Arsenal ta saye shi, a watan Janairu na 2018 kuma dan wasan ya koma Chelsea.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu