Isa ga babban shafi
Wasanni

FIFA ta kakabawa Chelsea takunkumin sayen 'yan wasa

Hukumar kwallon kafa ta Duniya FIFA, ta haramtawa kungiyar Chelsea sayen ‘yan wasa, har sai an kammala cin kasuwar hada-hadar cinikin ‘yan wasan guda biyu nan gaba.

Allon da ke nuna alamar hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA a harabar hedikwatarta da ke birnin Zurich na kasar Switzerland.
Allon da ke nuna alamar hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA a harabar hedikwatarta da ke birnin Zurich na kasar Switzerland. REUTERS/Arnd Wiegmann
Talla

Hukuncin na nufin Chelsea ba za ta sake sayen ‘yan wasa ba, har sai an shiga shekarar 2020, ko da yake kungiyar na da damar saida nasu ‘yan wasan.

FIFA ta kakabawa Chelsea takunkumin cinikin ‘yan wasan ne, bayan samunta da laifin saba ka’idar kulla yarjejeniya da wasu kananan ‘yan wasa da shekarunsu suka gaza kai ka’idar FIFA, da ta basu damar rattaba hannu kan yarjejeniya da wata kungiya.

Bayaga kakaba mata takunkumin cinikin ‘yan wasan, FIFA ta ci tarar Chelsea, dala dubu 600, sai dai kungiyar tana da damar daukaka kara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.