Kamaru za ta kara da Comoros ranar juma'a
Mai horar da kungiyar kwallon kafar Kamaru Clarence Seedorf ya gayyaci Paul Georges Ntep dan wasa mai shekaru 26 da ya taba buga wasa a Faransa da kungiyar Faransa a wasar sada zumunci da kuma ya yi na’am da tayi da Kamaru ta yi masa.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Ranar Juma’a dai ne Kamaru za ta karawa da kungiyar kwallon kafar tsibirin Comores dangane da neman tikitin shiga gasar cin kofin Afrika na shekara ta 2019 da Kamaru za ta dau nauyin shiryawa.
Daga cikin yan wasa da Clarence Seedorf ya gayyato za mu iya zana masu tsaron gida Fabrice Ondoa, Andre Onana,Carlos Kameni, yan wasan baya Fai Collins, Ngadeu Ngadjui,Oyongo Bitolo,Yaya Banana,Jerome Onguene, Gaetan Bong, Allan Nyom, kar mu manta da yan wasa kamar su Kunde Malong, Fabrice Olinga, Vincent Aboubacar, Karl Toko da sauren su.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu