Isa ga babban shafi
Wasanni

Jamus ta doke Najeriya a wasan farko na gasar cin kofin duniya

Tawagar kwallon kafar Najeriya ta mata ta Falconets, ta yi rashin nasara a wasan farko da ta fafata tsakaninta da Jamus a gasar ci kofin duniya na mata na ‘yan kasa da shekaru 20, da Faransa ke karbar bakunci.

'Yan wasan Najeriya na Falconets, yayin fafatawa da takwarorinsu na Jamus.
'Yan wasan Najeriya na Falconets, yayin fafatawa da takwarorinsu na Jamus. Richard Wolowicz/Getty Images
Talla

Jamus ta samu nasara kan Najeriya da 1-0 (ci daya mai ban haushi) ne ta hannun ‘yar wasanta Stefanie Saunders a wasan da suka fafata a yau litinin 6 ga watan Agusta, 2018.

Kasashen da Najeriya za ta fafata da su a wasannin gaba na matakin rukuni, sun hada da China da kuma Haiti.

A sauran wasannin da aka fafata a yau Litinin, China ta samu nasara kan Haiti da kwallaye 2-1, sai kuma Spain da ta lallasa Paraguay da kwallaye 4-1.

Sauran sakamakon wasannin da aka yi na farko a ranar Lahadi, sun hada da fafatawa tsakanin Faransa da Ghana, inda ‘yanmatan Faransar suka casa na Ghana da kwallaye 4-1.

Holland kuwa ta samu nasara kan New Zealand da kwallaye 2-1.

Gasar wadda aka soma ta a ranar lahadi 5 ga watan Agusta za ta kare a ranar 24 ga watan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.