Isa ga babban shafi
Wasanni

Sabon raunin da Neymar ya samu ya tayar da hankalin 'yan Brazil

Dan wasan gaba na Brazil Neymar, ya fice daga filin da suke asataye a jiya Talata yana dingishi, abinda ya tayar da hankalin tawagar kwallon kafar kasar, da ke shirin tunkarar wasanta da Costarica a ranar Juma’a mai zuwa.

Neymar tare da daya daga cikin likitocin tawagar 'yan wasan Brazil, yayin da suke ficewa daga fili, mintuna 30 bayan soma atasaye.
Neymar tare da daya daga cikin likitocin tawagar 'yan wasan Brazil, yayin da suke ficewa daga fili, mintuna 30 bayan soma atasaye. ADRIAN DENNIS / AFP/GETTY IMAGES
Talla

Kakakin hukumar kwallon kafa ta Brazil, Vinicius Rodrigues, ya tabbatar da cewa Neymar ya fice daga filin atasyen ne sakamakon ciwo da zogi da yake ji a idon sawunsa na kafar dama.

Rodriguez ya ce, jerin ketar da ‘yan wasan Switzerland suka rika yi wa Neymar wasan da suka 1-1 da Brazil ne ya janyo wa dan wasan samun raunin.

Kakakin hukumar kwallon ta Brazil, ya kara da cewa, raunin da Neymar ya samu, ba a wurin da ya karya kasusuwan kafarsa a watan Fabarairu, ya sake samu ba, raunin da ya tilasta masa hutun sama da watanni 3.

Ana sa ran a gobe Alhamis Neymar zai fito atasaye, kafin daga bisani su tafi zuwa birnin Saint Petersburg, domin fafatawa da Costarica a ranar Juma’a.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.