Isra'ila ta zargi Falasdinawa da firgita 'yan wasan Argentina
Hukumar kwallon kafa ta Isra’ila, ta ce zata shigar da karar takwararta ta yankin Falasdinu gaban hukumar FIFA, bisa zarginta da tursasawa tawagar kwallon kafar Argentina, soke wasan sada zumuncin da aka shirya zasu buga a birnin Kudus, ranar Asabar mai zuwa.
Wallafawa ranar:
Shugaban hukumar kwallon kafa ta Isra’ila Rotem Kamer, ya zargi takwaransa na Falasdinu Jibril Rajoub da yin barazana ga rayuka da kuma iyalan ‘yan wasan Argentina, duk da cewa babu wata kwakkwarar shaida kan zargin da ya bayyana.
Rahotanni sun ce shugaban hukumar kwallon kafa na yankin Falasdinu, Jibril Rajoub, ya bukaci Lionel Messi da ya jagoranci ‘yan wasan Argentina wajen kauracewa wasan sada zumuncin, in kuwa ba haka, zai umurci Falasdinawa masoya kwallon kafa su kone dukkanin rigunan da ke dauke da sunansa.
Sai dai a nata bangaren hukumar kwallon kafa ta Argentina ta ce, ta soke buga wasan sada zumuncin da Isra’ila ne a birnin na Kudus, saboda gano cewar wasan na tattare da manufar siyasa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu