Isa ga babban shafi
wasanni

Buhari ya gana da Super Eagles kan gasar kofin duniya

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya shaida wa tawagar kwallon kafar kasar, wato Super Eagles cewa, nauyin farin ciki ko kuma bakin cikin ‘yan kasar da yawansu ya haura miliyan 180 ya rataya a kanta a gasar cin kofin duniya a Rasha.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da mataimakinsa Yemi Osinbajo tare da tawagar Super Eagles a fadar Aso Rock a Abuja
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da mataimakinsa Yemi Osinbajo tare da tawagar Super Eagles a fadar Aso Rock a Abuja RFI/Kabir Yusuf
Talla

Shugaba Buhari wanda ya gana da ‘yan wasan na Super Eagles a yau gabanin tafiyarsu zuwa Rasha don wakiltan kasar ya ce, babu abin da ke hada kan ‘yan kasar kamar wasan kwallon kafa.

Buhari ya bukaci tawagar ta Super Eagles da ta buga wasa cikin tsanaki da kuma lashe kofin duniyar.

A bangare guda, tawagar ta Super Eagles ta rage yawan sunayen 'yan wasan da za su wakilce ta Rasha daga 30 zuwa 25

Kocin tawagar Gernot Rohr ya shaida wa Stephen Eze da Dele Ajiboye da Junior Lokosa da Uche Agbo cewa ba za a bukace su a Rasha ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.