Shirin duniyar wasanni na wannan makon tare da Abdurrahman Gambo Ahmad ya tattauna ne kan wasu muhimman batutuwa uku a duniyar tamaula da suka hada da kawo karshen aikin Arsene Wenger a matsayin kocin Arsenal a cikin tsawon shekaru 22 da kuma batun fafutukar kasashen da ke neman izinin daukar nauyin gasar cin kofin duniya ta 2026. Sai kuma matakin da hukumar kwallon kafa ta duniya wato FIFA ta dauka na ladabtar da Rasha saboda kalaman nuna wariyar launin fata akan wasu 'yan wasa bakaken fata.
Sauran kashi-kashi
-
Ci gaban da aka samu a wasan damben gargajiya a Najeriya
Shirin 'Duniyar Wasanni' na wannan makon tare da Khamis Saleh ya maida hankali ne kan irin ci gaban da aka samu a bangaren wasan damben gargajiya a Najeriya.11/03/202409:59 -
Yadda aka kammala zangon farko na gasar kwallon kafa ta Firimiyar Najeriya
Shirin awanan lokaci zai nazari game da yadda zangon farko na gasar Firimiyar Najeriya ya kammala, inda tuni aka juya zagaye na biyu na gasar ta kwararru.Shirin ya kuma duba batun soma gasar a kan lokaci da kuma batun daukar nauyi, sai kuma batun rashin ingancin filaye, baya ga kuma karanchin samun bayanan ‘yan wasan da ke taka leda a gasar.Latsa alamar sauti don sauraron shirin:04/03/202410:00 -
Yadda Ivory Coast ta lashe kofin AFCON bayan ta doke Najeriya
A daren jiya Lahadi ne aka kammala gasar lashe kofin Afrika AFCON karo na 34 da Ivory Coast ta karbi baukunci kuma daga bisa ta lashe gasar. Najeriya ce ta fara zura kwallon farko ta hannun William Ekong tun kafin a tafi hutun rabin lokacin, sai dai bayan dawowa ne tawagar ta Elephants ta farke ta hannun Kesse kafin daga bisani a minti na 81 ta kara kwallo ta hannun Sebestin Hallar wacce ta bata nasara.12/02/202409:58 -
Yadda wasannin zagayen Kwata final suka kaya a gasar AFCON
Shirin 'Duniyar Wasanni' na wannan lokacin yayi nazari ne akan wasannin matakin dab da na kusa da na karshe wato na zagayen Kwata final da aka yi a gasar AFCON.05/02/202410:00 -
Matakin zagayen dab da na kusa da na karshe a gasar lashe kofin Afrika AFCON
A yau Juma’a nan ce dai za a fara buga wasannin zagen dab da na kusa da na karshe a gasar lashe kofin Afrika AFCON da ke gudana a kasar Ivory Coast.Za kuma a fara karawar ne tsakanin Najeriya da Angola karfe shida agogon Najeriya, kafin da misalign karfe 9 a buga wasa tsakanin DR Congo da Guinea.A wasannin gobe Asabar, akwai karawa tsakanin Mali da Cote d’Ivoire sai kuma Cape Verde da Afrika ta Kudu.02/02/202409:59