Isa ga babban shafi
wasanni

Leceister City za ta maye gurbin Mahrez da Hazard

Rahotanni na cewa, Leicester City na duba yiwuwar sauya dan wasanta na gaba Riyad Mahrez da dan uwan Eden Hazard, wato Thorgan Hazard da ke taka leda da Borussia Monchengladbach a Jamus.

Riyad Mahrez na bakin-cikin rashin zuwa Manchester City daga Leceister City
Riyad Mahrez na bakin-cikin rashin zuwa Manchester City daga Leceister City dailymail
Talla

A watan jiya ne aka bukaci Mahrez da ya jajirce don ganin ya koma Manchester City da taka leda amma Leiceter City ta dage kan cewa, ba za ta sallama dan wasan ba akan farashin da ya yi kasa da Pam miliyan 90.

Tun daga wannan lokacin, Mahrez dan asalin Algeria ke kaurace wa atisaye tare da kungiyar don nuna bakin-cikinsa akan abin da ta yi ma sa na hana shi zuwa Manchester City.

Tuni dai mahukuntan kungiyar suka fara nazarin maye gurbin Mahrez da kwararren dan wasa kuma ana kyautata zaton Thorgan Hazard za ta dauko.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.