Isa ga babban shafi
wasanni

Kwamitin La Liga zai binciki Pique na Barcelona

Shugaban gasar La Liga ta Spain, Javier Tebas ya ce, hukumomin kwallon kafar kasar za su gudanar da bincike kan yadda dan wasan baya na Barcelona Gerard Pique ya nuna murnarsa ta barke kwallon da Espanyol da zura musu a karawar da suka yi a ranar Lahadi.

Gerard Pique na fuskantar barazanar haramcin wasanni uku nan gaba
Gerard Pique na fuskantar barazanar haramcin wasanni uku nan gaba REUTERS
Talla

Pique wanda ya barke kwallon ana dad da tashi wasan, ya sanya dan yatsarsa akan lebensa da nufin magoya bayan Espanyol su yi tsit da bakinsu, lamarin da ya harzuka magoyan bayan har suka mayar da zazzafan martani.

Matukar dai kwamitin gasar La Liga ya samu Pique da laifi, akwai yiwuwar haramta ma sa wasanni uku nan gaba.

Pique ya yi kaurin suna wajen nuna adawarsa da magoya bayan Espanyol, in da kuma yake yawan yaba musu magana, yayin da ya zargi magoya bayan da zagin iyalansa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.