Isa ga babban shafi
Wasanni

Jamus ta ci gaba da rike kanbinta a jadawalin FIFA

Jamus da Brazil sun ci gaba da rike matsayinsu na ɗaya da na biyu a jerin ƙasashen da suka fi iya shafa ƙwallon ƙafa a duniya.

Jamus ta ci gaba da rike matsayi na daya a kwallon kafa a duniya.
Jamus ta ci gaba da rike matsayi na daya a kwallon kafa a duniya. AFP/AFP/Archives
Talla

Hakan na ƙunshe ne a cikin sabon jadawalin ƙasashe masu buga ƙwallon ƙafa da hukumar FIFA ta fitar, a watan Nuwamba, 2018.

Portugal ce ta 3 a cikin jerin, yayin da Argentina ke a matsayi na 4, sai kuma Belgium a matsayi na 5.

Senegal wadda ke a matsayi na 23 a duniya ita ce ta ɗaya a nahiyar Afirka. Tunisia na biye mata a matsayi na 27 a duniya kuma ta biyu a Afirka, yayin da Masar ke a matsayi na 3 a Afirka.

Kamaru ce ta 7 a Afirka, sai Ghana a matsayi na 8, Najeriya kuma na a matsayi na 9, inda a duniya kuma take a matsayi na 51.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.