Isa ga babban shafi
Wasanni

Chelsea za ta kece raini da Barcelona

An hada ƙungiyoyi da za su kara a zagayen rukunin 16 na gasar zakarun nahiyar Turai inda Chelsea za su kece raini da Barcelona.

Dan wasan Barcelona Lionel Messi.
Dan wasan Barcelona Lionel Messi. Reuters
Talla

Ƙungiyar Chelsea ta fi samun nasara a kan Barcelona cikin karawa 12 da ƙungiyoyin biyu suka yi a baya, inda ta doke Barcelona sau 4, yayin da Barcelona ta doke Chelsea sau 3.

A ranar Litini ne aka hada ƙungiyoyin

Sauran wasannin da za a kara su ne:

Basel da Manchester City

Bayern Munich da Besiktas

Juventus da Tottenham

Porto da Liverpool

Real Madrid da PSG

Sevilla da Manchester United

Shaktar Donetsk da Roma

Za a buga wasannin karo na farko ne a ranakun 13 da 14 na watan Maris, 2017.

Ƙungiyoyi biyar ne daga Burtaniya suka samu nasarar zuwa zagayen na 16 a gasar ta zakarun Turai.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.