Zidane ya gargadi masu caccakar Cristiano Ronaldo
Kocin Real Madrid Zinedine Zidane ya yi gargadi, kan caccakar Cristiano Ronaldo da ke saran lashe kyautar Ballon d’or a cikin wannan makon karo na 5.
Wallafawa ranar:
Kwallaye 2 a cikin wasanni 10 na la liga Ronaldo ya zura a wannan kakar da suke fadi tashi, ganin cewa akwai ban-bancin maki 8 tsakaninsu da Barcelona da ke jan ragamar teburin.
Sai dai Ronaldo yana kan gaba wajen yawan kwallaye a zakarun Turai, inda ya zura kwallo 8 a wasanni 5 wanda Zidane ke saran a la liga ma zasu farfado.
Zidane ya ce 'daman a koda yaushe idan mutane basu samu yadda suke so ba sai suka da caccaka ya biyo baya.' Kallaman kocin na zuwa ne gabanni fafatawarsu na yau talata a Borussia Dortmund.
Shi ma karim Benzema a wannan kaka, kwallo na masa wuyar shiga raga. Abinda ya sa wasu irin kocin Valencia, Marceliono Garcia, ke cewa tawagar Madrid ta yi rauni a wannan kaka saboda rashin Alvaro Morata da James Rodriguez da Pepe.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu