Isa ga babban shafi
Kanya

Komitin Kwallon Kafa Na Africa Ya Hana Kenya karban Gasan cin Kofi Na 2018.

Bayan wani taron komitin zartaswa dake shirya gasan wasan kwallon kafa na cin kofin Zakaru na nahiyar da aka yi a Accra na kasar Ghana,  an dakatar da kasar Kenya daga karban bakuncin gasan kwallon kafa na cin kofin nahiyar a shekara ta 2018.

Wasu shugabannin da suka halarci wasan kwallon kafa da aka buga a shekara ta 2015. A ciki akwai shugaba Alassane Ouattara na Ivory Coast
Wasu shugabannin da suka halarci wasan kwallon kafa da aka buga a shekara ta 2015. A ciki akwai shugaba Alassane Ouattara na Ivory Coast rfi
Talla

Ahmad Ahmad daga kasar Madagascar, wanda shine  shugaban komitin ya bayyana cewa tafiyar hawainiya wajen shirin gasan wasannin ya sa aka kwace daga kasar Kenya.

Komitin ya gano cewa duk da cewa tsakanin watan Janairu zuwa Fabrairu za’a yi gasan, hukumomi a kasar Kenya sun sami kammala filin wasa daya ne kawai daga cikin filayen wasanni hudu da aka tsara za'a yi wasan a ciki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.