Isa ga babban shafi
wasanni

Za a kara tsakanin Ghana da Najeriya don daukar kofin WAFU

A jiya alhamis aka buga wasannin zagayen gaf da na karshe domin daukar kofin kwallon kafa na yammacin Afrika wato WAFU, a gasar da ake ci gaba da yi a birnin Cape Coast na kasar Ghana.

MiaI horas da Super Eagles, Gernot Rohr
MiaI horas da Super Eagles, Gernot Rohr pbplusoilandgas
Talla

A wasan na jiya, Nigeria ta doke Jamhuriyar Benin ci daya mai ban haushi, yayin da Ghana ta doke Niger ci biyu da nema.

Za a yi fafatawar karshe ne a ranar lahadi domin daukar wannan kofi tsakanin Ghana da Nigeria, yayin da Niger za ta fatafa da jamhuriyar Benin domin neman matsayi na uku a tsakaninsu.

 

Ana bayar da tukuicin dalar Amurka dubu dari daya ga kasar da ta dauki wannan kofi, sai kuma dala dubu 50 ga wadda ta zo a matsayin ta biyu, yayin da kasar da ta zo ta uku ke samun kyautar dala dubu 25.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.