Isa ga babban shafi
Wasanni

Najeriya ta lashe gasar kwallon kwando ta nahiyar Africa

Tawagar kwallon Kwando ajin mata da ke wakiltar Najeriya, wato D’Tigress, ta samu nasarar lashe kofin gasar kwallon Kwando ta nahiyar Africa, karo na uku, da ta gudana a babban birnin Mali, Bamako.

Tawagar 'yan wasan kwallon kwando ta Najeriya D'Tigress da ta lashe kofin gasar ta nahiyar Afrika a Bamako, Mali.
Tawagar 'yan wasan kwallon kwando ta Najeriya D'Tigress da ta lashe kofin gasar ta nahiyar Afrika a Bamako, Mali. Punch
Talla

Najeriya ta samu nasarar ce bayan lallasa kasar Senegal da kwallaye 65 da kuma 48 a wasan karshen da suka fafata a jiya Lahadi.

Ko wasan rukuninsu na B da suka fafata a farkon wannan gasa, ‘yan matan kwallon kwandon na Najeriya, sun lallasa tawagar Senegal da kwallaye 58 da kuma 54.

Ba dai a wannan karon bane kadai Najeriya ke doke Senegal a wasan karshen na cin kofin kwallon kwandon nahiyar Afrika ajin mata, domin a shekara ta 2005 D’ Tigress din sun lallasa Lionesses din na Senegal da kwallaye 64 da kuma 57 a garin Abuja.

Yanzu haka dai Najeriya na da kofunan wannan gasa har uku, shekara ta 2003, 2005, da kuma wannan ta 2017.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.