Isa ga babban shafi
Wasanni

Gasar wasannin kasashe renon Faransa a birnin Abidjan

Wannan juma’a ake bude gasar wasannin kasashen renon Faransa karo na 8 a kasar Cote d’Ivoire, wasannin da za a ci gaba da gudanarwa har zuwa ranar 30 ga wannan wata na yuli.

Tambarin gasar wasannin kasashe renon Faransa a birnin Abidjan 2017
Tambarin gasar wasannin kasashe renon Faransa a birnin Abidjan 2017 Sia KAMBOU / AFP
Talla

Shekaru 30 da farawa, sai a wannan ne Cote d’Ivoire ke daukar nauyin shirya gasar, inda ‘yan wasa daga kasashe kusan 80 suka hallara.

Za a bude gasar ce a daidai lokacin da kasar ke farfadowa daga matsalar yajin aiki, boren soji da kuma nuna wa duniya cewa kasar za ta iya daukar nauyin wasannin kasa da kasa, a matsayinta na kasar da za ta shirya gasar neman kofin kwallon kafar Afirka a 2021 idan Allah ya kai mu.

Cote d’Ivoire ta zama kasa ta hudu da ke daukar nauyin wannan gasa ta Francophonie a Afirka, bayan ga birnin Rabat na kasar Maroko a 1989, Antananarivo na Madagascar a 1997, sai Yamai a jamhuriyar a 2005.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.