An fitar da jadawalin gasar kwallon kwando ta nahiyar Africa
Tawagar ‘yan wasan kwallon Kwando ta Najeriya D’Tigers, ta tsinci kanta cikin rukunin farko, a gasar kwallon kwandon ta Nahiyar Africa, wadda za’a fara daga ranar 8 ga Satumba, zuwa 16 ga watan, a kasashen Senegal da Tunisia.
Wallafawa ranar:
Najeriya, wadda ke da kofin gasar, zata fafata da kasashen Jamhuriyar Kongo, Mali da kuma Cote D’Ivoire.
A rukunin B kuwa kasashen Angola, Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya, Morocco da kuma Uganda ne zasu fafata, rukuni na uku kuwa an hada kasashen Tunisia, Guinea, Rwanda da kuma Kamaru.
Yayinda a rukunin karshe aka hada kasashen Mozambique, Masar, Afrika ta Kudu, da kuma Senegal.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu