Kwallon kafa
Dani Alves ya koma PSG
Paris Saint Germain ta gabatar da Dani Alves dan wasan Brazil da ta karbo daga Juventus inda ya sanya hannu kan yarjejeniyar shekaru biyu da kungiyar.
Wallafawa ranar:
Talla
Dan wasan ya ce yana fatar kafa tarihi idan ya lashe kofin zakarun Turai da Paris Saint Germaine.
An yi zaton dan wasan zai koma Manchester City City domin sake haduwa da tsohon kocinsa Pep Guardiola da ya horar da shi a Barcelona.
Amma Alves ya yi watsi da bukatar bayan PSG ta taya shi fiye da kudaden da City ta ce zata bashi.
Dan wasan zai karbi kudi euro miliyan 14 a duk shekara.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu